1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Afirka ta Kudu ba za ta halarci G20 na 2026

Abdourahamane Hassane
December 4, 2025

Afirka ta Kudu ta sanar da cewar za ta ɗauki hutun shekara ɗaya daga halartarta a taron G20 bayan da Donald Trump ya yanke shawarar cireta daga cikin taron da za a gudanar a Amurka a shekarar ta 2026.

https://p.dw.com/p/54lnZ
Italien Rom | G20 Gipfel | Gruppenfoto
Hoto: Yara Nardi/REUTERS

Kakakin shugaban Afirka ta Kudu Vincent Magwenya ya ce Pretoria za ta janye daga jerin tarurrukan  na G20 na shekara ta 2026.

Kuma za ta ci gaba da shiga lokacin da aka mika wa Birtaniya ragamar gudanar da taro a  shekara ta 2027.Dangantaka tsakanin Washington da Pretoria ta sukurkurce tun bayan da Donald Trump ya sake koma Fadar White House.

Washington na zargin Afirka ta Kudu da tursasawa  Afrekaner wani bangaran al ummar kasar 'yan asalin Turai na farko a Afirka ta Kudun , abin da pretoria ta musunta.