1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sace wasu mutanen a Jihar Kwaran Najeriya

Abdourahamane Hassane
November 25, 2025

Kwamishinan 'yan sanda na Jihar Kwara ya shaida cewar wasu 'yan bindiga ne suka yi garkuwa da su.

https://p.dw.com/p/54GDf
'Yan sanda a Eruku na neman wadanda aka sace
'Yan sanda a Eruku na neman wadanda aka saceHoto: Abdullahi Dare Akogun/REUTERS

 Kwamishinan 'yan sanda na Jihar Kwara Adekimi Ojo ya shaida cewar wasu mutanen dauke da makamai sun yi harbi sama

kafin su yi awan gaba da mutanen goma a kauyen Isapa, wanda ya ce galibin wadanda aka sacen manoma ne da yara .

Wannan satar mutane na zuwa ne a dai-dai lokacin da ƙasar da ta fi yawan jama'a a  Afirkake fuskantar sabon salon garkuwa da mutane.

Makon da ya gabata, an yi garkuwa da masu ibada 35 a lokacin wani hari da aka kai wa wata coci mai nisan kilomita 20 daga Isapa, a ƙauyen Eruku.