1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An yi yunkurin cafke wani 'dan fafutukar Tanzaniya a Nairobi

February 24, 2026

Kungiyar Amnesty ta ce an yi yunkurin sace wani 'dan fafufutar kare hakkin 'dan adam, to amma ya tsallake rijiya da baya.

https://p.dw.com/p/59ImS
Shugabar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan
Shugabar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan Hoto: Ericky Boniphace/AFP

Dan fafutukar mai suna Mshabaha Mshabaha Hamza, na daya daga cikin mutanen da suka yi kaurin suna wajen sukar manufofin gwamnatin Tanzaniya, kan yadda ta yi amfani da karfin tuwo wajen murkushe masu zanga-zanga, a lokacin da aka gudanar da babban zaben kasar. Mutane sama da 2,000 suka mutu a yayin zanga-zangar. Ana dai zargin gwamnatin Tanzaniya da kin fitar da rahoton ta'asar da aka yi a yayin boren.

Karin bayani:Amnesty ta zargi Tanzania da batar da gawarwakin 'yan adawa

A shekarar 2024, an sace madugun adawar Uganda Kizza Besigye a birnin Nairabi, inda aka gurfanar da shi a kotun Kampala kan zargin cin amanar kasa. Kazalika a watan Janairun 2025, an sace wata lauya mai fafutukar kare hakkin bil Adama, Maria Sarungi Tsehai, a birnin Nairobi, to amma daga bisani ta shaki iskar 'yanci bayan kwarmaton da manema labarai da kuma kungiyoyin kare hakkin bila Adama suka yi na labarin cafke ta.