1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Al'aduAfirka

Azumin Musulmi ya zo lokaci guda da Lent na Kirista

Abdullahi Maidawa Kurgwi Mouhamadou Awal
February 18, 2026

Al’ummar Musulmi sun fara azumin watan Ramadana na bana, rana guda tare da mabiya addinin Kirista da ke Azimin Lent. Ko wasu darusa ne ke akwai ga mabiya addinan biyu?

https://p.dw.com/p/58yUF
Musulmi na ninka ibada a lokacin azumin watan Ramadana
Musulmi na tsananta ibada a lokacin azumin watan RamadanaHoto: DW

Watan azumin Ramadana ya kasance lokacin da al'umma ke kara kusantar da kansu ga ubangiji don samun ceto da rahamarsa. A ranar Laraba 18.02.2026 ne al'ummar Musulmi suka fara  Azumin Ramadana da kan iya kai kwanaki 29  ko 30.

Su ma mabiya addinin Kirista sun fara azumin Lent,  Inda sukan shafe kwanaki 40 suna gudanar da shi. Rev. Auta Yohana, mataimakin  magatakardar  mujami'ar  COCIN Jos Jarawa a jihar Filato ya ce manufar  yin Azumin Lent ga mabiya addinin kirista shi ne: "don tunawa da lokacin da Yesu ya mutu har ya tashi daga kabari... Ana kuma tuna rayuwa don ba har abada aka zo ba. Sannan ana sadaka da taimaka wa gajiyayyu da karfinsu bai kai ba."

Bambancin azumin Ramadana da Lent

Baya ga kaurace wa wasu naukan abinci, Kiristoci na zuwa wuraren ibada a lokacin Lent
Baya ga kaurace wa wasu naukan abinci, Kiristoci na zuwa wuraren ibada a lokacin LentHoto: DW

A bangare guda, malaman addinin Musulunci na yin amfani da azumi wajen fadakar da al'ummar Musulmi fa'idar da ke tattare da  watan Ramadana, musamman wajen kara fuskantar ayyukan ibada da kuma nisanta kai daga munanan ayyuka. 

Karin bayani: Azumi: kamanceceniyar dabi'u tsakanin Kirista da Musulmi

Nazir Shazali Ali, daya daga cikin malaman Musulunci a garin Jos na jihar Filato ya ce akwai koyarwa ga Musulmi a cikin watan  Ramadana. Ya ce: "Allah ya yi mana wannan domin mu kusance shi... Shi azumi an yi shi ga dukkanin al'umomi na annabawa tun daga kan annabi Nuhu."

 A cikin azumin Ramadana,  al'ummar Musulmi na zamantowa cikin ibada, tare da kame baki daga ci ko sha, tun daga ketowar alfijir har zuwa faduwar rana. Yayin da a gefe guda, mabiya addinin kirista kan kaurace wa wasu  na'ukan abinci har na tsawon kwanaki 40  domin kyautata tsarki cikin zukatansu .

Kiraye-kirayen taimaka wa marasa karfi

Musulmi da Kiristoci na azumi a lokaci guda a bana
Musulmi da Kiristoci na azumi a lokaci guda a banaHoto: Pond5 Images/IMAGO

Rev. Yakubu Pam, Shugaban kungiyar mabiya addinin kirista ta kasa reshen jihohin arewacin Najeriya ya yi nasiha ga mabiya addinan guda biyu. Ya ce: "Ubangiji ya ji tausayi, ya wanke mana duk kuskure da muka yi. Akwai ma wadanda za ka gan su a kan titi suna adu'a Allah ka taimake ni."

Karin bayani:Taimakon Azuni a Najeriya

Shugabanin daga bangaren addinan biyu na ci gaba da kiraye-kiraye wajen ganin cewar al'umma masu hannun baiwa sun taimaka wa  gajiyayyu domin su samu  saukin gudanar da ibada.