1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fafaroma Leo ya kadu da sace dalibai a Najeriya

November 23, 2025

Jagoran darikar Katolika na duniya, Fafaroma Leo XIV ya yi kira da a ceto sama da dalibai 300 da aka yi garkuwa da su a makarantar cocin Katolika ta jihar Neja a Najeriya.

https://p.dw.com/p/544oN
Jagoran darikar Katolika na duniya, Fafaroma Leo XIV
Jagoran darikar Katolika na duniya, Fafaroma Leo XIVHoto: Filippo Monteforte/AFP

Fafaroma Leo ya nuna matukar kaduwarsa game da sace-sacen malaman addinini da dalibai a kasashen Najeriya da Kamaru. Shugaban darikar Katolikan ya kuma bukaci jama'a da su yi wa yaran maza da mata da aka sace addu'a, tare da fatan mujami'u da kuma makarantu za su ci gaba da kasance wuraren da ke da tsaro.

Karin bayani: Wane hali iyayen dalibai ke ciki a Kebbi?

A ranar Litinin ce 'yan bindiga suka kai hari wata makarantar kwana ta mata a jihar Kebbi inda suka sace dalibai 25.Da safiyar ranar Juma'a suka sace wasu daliban a makarantar St Mary da ke jihar Neja. Har yanzu Najeriya na ci gaba da jimamin sace 'yan matan Chibok fiye da 300 da mayakan Boko Haram suka yi shekaru fiye da 10 da suka gabata, 'yan matan da har yanzu ba a ga wasu ba.