1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Harin Isra'ila a Sana'a babban birnin Yemen ya halaka mutane

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
August 25, 2025

Harin na Isra'ila na zama ramuwar gayya ga hare-haren da Houthi ke kai wa jiragen ruwan Isra'ila a kogin Baharmaliya.

https://p.dw.com/p/4zRiv

Harin Isra'ila a Sana'a babban birnin Yemen ya halaka mutane 6 a jiya Lahadi, tare da jikkata wasu 86, kamar yadda 'yan tawayen Houthi masu samun goyon bayan Iran suka tabbatar.

Harin na Isra'ila na zama ramuwar gayya ga hare-haren makamai masu linzami da Houthi ke kai wa jiragen ruwan Isra'ila masu ratsawa ta kogin Baharmaliya, wanda Houthin ke ikirarin cewa tana ramawa Falasdinawan Gaza ne.

Karin bayani:Jamus ta bukaci a dakatar da yunwa a Gaza

Wasu hotuna da ma'aikatar tsaron Isra'ila ta wallafa da ranar jiya Lahadi, sun nuna yadda Firaminista Benjamin Netanyahu da ministan tsaro Israel Katz da kuma babban hafsan sojin kasar Eyal Zamir ke nazartar yadda harin na Yemen ke gudana.