Jakadan Sudan ya caccaki rawar da EU ke takawa a yakin Sudan
October 30, 2025
Jakandan ya furta hakan a wani taro da aka gudanar a birnin Brussels na kasar Belgium, inda ya bukaci tallafin kungiyar EU da sauran kasashen duniya wajen ganin cewa sun dauki mataki kan rundunar kar-ta-kwana ta RSF da kuma wadanda ke goyon bayan su daga kasashen ketare.
Karin bayani:Shin ana iya kawo karshen rikicin Sudan?
Ambassada Aldelbagi Kabeir na daga cikin jami'an gwamnatin da ke bangaren Janar Abdel-Fattah Burhan da Firaminista Kamil al-Taib Idris, wadanda kasashen duniya ta amince dasu a matsayin halastattun shugabannin Sudan.
Karin bayani:EU ta fusata kan ta'asar RSF a el-Fasher
A baya bayan nan dai mutuna sama da 30,000 suka kauracewa yankin el-Fasher, sakamakon kwace iko da RSF ta yi da kuma luguden bama-bamai da hare-haren kan mai uwa da wabi da take kai wa a yankin.