Jamus da Brazil na neman kara karfin dangantaka
April 19, 2026
Shugaban gwamnatin Jamus, Friedrich Merz na shirin karbar bakuncin shugaban Brazil Luiz Inácio Lula da Silva a birnin Hannover. Ana sa ran shugabanin biyu su bude taron baje kolin kasuwar masana'antu mafi girma a duniya a birnin. A ranar Litinin ake sa ran gwamnatocin kasashen biyu za su gudanar da taron tuntuba da nufin kara karfafa alaka, a bangarorin kasuwanci da tsaro da ci-gaban fasaha da bincike da kuma kare yanayi.
Karin bayani: Jamus na neman kwararru daga Brazil
Za kuma su tattauna kan dokokin kasa da kasa, ciki har da matakin Amurka a kan Iran da Venezuela da kuma Cuba. Shugaba Lula da ke neman kujera ta dindindin a kwamittin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, na fatan yin fito na fito da karfin ikon Shugaba Trump a siyasance.
A lokacin da yake tattaunawa da jaridar Der Spiegel, Lula ya ce ba a zabi Trump a matsayin basaraken duniya ba, don haka bai kamata ya ci gaba da yin barazana ga kasashe da yaki ba.