SiyasaAfirka
Masu Aikin Sa Kai Sun Mutu Sakamakon cutar Ebola a Kongo
May 23, 2026
Talla
Kungiyar ta ce mutanen uku na aiki ne a garin Mongbwalu da ake ganin shi ne inda cutar tafi kamari. Sun kamu da Ebolan ne yayin aikin daukar gawarwaki a wani aikin jin kai
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce ya zuwa yanzu an tabbatar da mutane 82 sun kamu da cutar a Kongo, yayin da mutane bakwai suka mutu. baya ga zargin akwai daruruwan mutane da suka kamu har ila yau.
Kungiyar Red Cross din ta ce har yanzu akwai damar dakile yaduwar cutar, amma lokaci na kurewa, yayin da ake ci gaba da wayar da kan al'umma kan yadda za su kare kansu daga cutar.