1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Mojtaba Khamenei ya zama jagoran addinin Iran

March 9, 2026

Nadin Mojtaba Khamenei a matsayin sabon jagoran addinin Iran ya zo a lokacin da toshe mashigin Hormuz ya jefa kasuwannin hannayyen jari a yankin Asiya cikin wadi na tsaka mai wuya.

https://p.dw.com/p/5A1uE
Mojtaba Chamenei, sabon jagoran addinin Iran
Mojtaba Chamenei, sabon jagoran addinin IranHoto: Iran state TV/AP Photo/picture alliance

Mojtaba Khamenei ya gaji mahaifinsa Ayatullah Ali Khamenei a matsayin jagoran addini na Jamhuriyar Musuluncin Iran, kwanaki tara bayan kisan tsohon jagoran duk kuwa da gargadin da Isra'ila da Amurka suka yi na ci gaba da farautar wanda za a nada.

Majalisar manyan malaman Iran mai membobi 88 ce ta zabi Mojtaba Khamenei mai shekaru 56 da haihuwa a matsayin sabon jagora saboda alakarsa da dakarun juyin juya halin Musulumcin kasar, wadanda take yanke suka yi masa mubaya'a bayan nadinsa.

Sa'o'i kalilan kafin sanar da nadin Mujtaba Khamenei, shugaban Amurka Donald Trump na Amurka ya yi gargadin cewa sabon jagoran da Iran za ta nada ba zai yi dogon zamani ba inda bai ba tare da amincewarsa ba, yayin a gefe guda Isra'ila ta sha alwashin ganin bayan wanda zai gaji marigayi Ayatullah Ali Khamenei.

Amurka da Isra'ila sun sake far wa Iran da Lebanon

Yarima Mohammed bin Salman ya yi tir da hare-haren Iran kan kasashen Musulmi
Yarima Mohammed bin Salman ya yi tir da hare-haren Iran kan kasashen MusulmiHoto: Win Mcnamee/Getty Images

Saudiyya ta gargadi Iran kan wuce gona da iri a hare-hare

Yayin da yakin yankin Gabas ta Tsakiya ke cika kwanaki 10 da barkewa, Saudiyya ta fidda wata sanarwa inda ta yi Allah wadai da hare-haren wuce gona da iri da Iran ke kai wa kasar da makwabtanta na yankin Golf.  

A cikin sanarwar ma'aikatar harkokin wajen Saudiyya ta fitar, ta nanata cewa ba za a amince da wadannan hare-hare na ramuwar gayya da Iran ke ci gaba da kai wa kasashen Musulmi ba. Wannan na zuwa ne a yayin da a wannan safiya Hadaddiyar Daular Labarawa ta ce ta wayi gari da sabbin hare-haren makamai masu linzami daga Iran.

A gefe guda Isra'ila ta ce ta kai sabbin samame kan mayakan Hezbollah masu alaka da Iran a gabashin Lebanon inda ake gwabza kazamin fada. 

A daidai wannan lokaci ma'aikatar harkokin wajen China ta ce manzonta na yankin Gabas ta Tsakiya ya yi kira da a kai zuciya nesa a yayin ganawar da ya yi da babban jami'in diflomasiyyar Saudiyya.

Iran ta toshe mashigin Hormuz mai tasiri ga arzikin duniya

Toshe mashigin Hormuz na barazana ga tattalin arzikin kasashen Asiya
Toshe mashigin Hormuz na barazana ga tattalin arzikin kasashen AsiyaHoto: Amr Alfiky/REUTERS


Faranshin gangar mai ya yi tashin gwauron zabo

Farashin gangar mai ya karu da kashi 30% a cikin sa'o'i kalilan a safiyar yau Litinin, inda ya zarta dala 115. Wannan tashin farashi dai an dade ba a ga irinsa ba sakamaon fargaba da ta mamame kasuwannin danyen mai saboda toshe mashigin Ormuz da Iran ta yi da kuma lalata cibiyoyin samar da makamnashi.  

Farashin danyen man Amurka na WTI ya karu da kashi 25,3,% inda ake sayar da ganga guda a kan dala 113,90, yayin da shi kuma danyen mai na Brent da ya fi tagomashi a kasuwanni ya tsahi da kashi 22,99%, lamarin da ya sa ake sayar da kowacce gangar a kan dala 114.

Ko da yake mamayar da Rasha ta kai wa Ukraine ta haifar da tashin farashin gangar danyen mai zuwa dala 130,50 a farkon watan Maris na 2022,  sai dai lamarin bai kai munin irin na wannan karon ba in ji masana. 

Tuni a yankin Asiya mai dogaro kacokan da danyen mai da iskar gas da ke fitowa daga kasashen yankin Golf, kasuwannin hannayen jari suka fara faduwa sakamakon hauwawar farashi man fetur.