Najeriya: INEC za ta yi wa Jam'iyyu 14 rajista
September 12, 2025
An dai dauki lokaci ana sa in sa bayan da wasu kungiyoyin siyasa har 171 suka nemi hukumar zaben INEC ta sahale musu rikidewa ya zuwa jam'iyyun siyasa a cikin tarayyar Najeriya, kafin wata sanarwar da a cikin ta hukumar ta ce 14 ne suka cancanta su zama jam'iyyun da za su taka rawa a fagen siyasar kasar.
INEC din dai ta sa kafa ta shure wasu bukatu 157 da ta ce basu cancanci rikidewa zuwa jam'iyyu ba.
Karin Bayani: Neman karuwar jam'iyyun siyasa a Najeriya
Ana dai kallon sabon matakin da kokarin wankan tsarki a bangaren hukumar zaben da sannu a hankali ta ke dada fuskantar rikicin iya tantance bukatu cikin fagen siyasar tarayyar Najeriyar.
Sabbabin jam'iyyun dai sun hada da African Transformation Party, da All Democratic Alliance, da Advance Nigeria Congress da kuma Abundance Social Party.
Sauran sun hada da African Alliance Party da Citizens Democratic Alliance da Democratic Leadership Alliance da kuma Grassroots Initiative Party.
Karin Bayani:Ko hadakar jam'iyyun adawa ne mafitar Najeriya?
Akwai kuma Green Future Party da Liberations Peoples Party da kuma National Democratic Party. Sai kuma National Reform Party da Patriotic Peoples Alliance da kuma Peoples Freedom Party.
A ranar laraba ta makon gobe ne INEc din tace za ta kamala tantance takardun sabbin jam'iyyun da ma ganawa da shugabannin su na riko