Nijar: Murna da wucewar motocin dakon kaya
February 9, 2026
Kimanin motocin dakon kaya 1600 ne na Nijar suka makale tsawon watanni a kan iyakar Benin da Najeriya bayan da kayayakin suka fito daga tashar Ruwan Cotonou saboda rufe rufe iyakar Nijar da Benin. Hukumomin Kwastam ko Douane na kasashen biyu sun yi wani zaman na musamman domin magance matsalar inda shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin barin motocin su wuce.
Karin Bayani: Binciken kaya da daga Najeriya zuwa Nijar
Daga Nashi bangare mai bai wa ministan kula da harkokin kasuwanci da masana'antu na kasar ta Nijar shawara Nayoussa Djimraou, ya ce batun kasuwanci abu ne da ya shafi al'umomin kasashe kai tsaye saboda haka akwai bukatar kawar da rashin jittuwa don dorewar kasuwanci tsakanin kasashen biyu.
Karin Bayani:Bambancin ra'ayi kan rashin bude wasu iyakokin Nijar
Ga masu sharhi kan harkokin siyasar kasa da kasa da tsaro irin su farfesa Dicko Abdourahamane Malamai na Jami'ar birnin Damagaram, wannan masalaha da aka samu abin jinjinawa ne ga shugabannin Najeriya da na Nijar da aka yi hakan da amincewarsu
Karin Bayani:Hare-hare kan motocin dakon kaya a Nijar
Abun jira agani dai shine ko wannan mataki zai dore ba tare da wani cikas ba? har ma da kasar Benin inda wasu daga cikin kayayakin yan kasuwar ta Nijar ke bi ta tashar ruwanta su ratsa Najeriya ta yankin Segbana na kasar Benin saboda rufe iyaka ta tsakanin Nijar da Benin