1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Rukunin farko na 'yan Najeriya sun dawo daga Afirka ta Kudu

June 11, 2026

Rukunin Farko Na 'yan Najeriya da aka kwaso daga Afirka ta Kudu sun isa birnin Lagos, bayan umarnin da gwamnati ta bayar na mayar da su sakamakon zanga-zangar adawa da bakin da ta rikide zuwa tashin hankali.

https://p.dw.com/p/5FD0y
Fasinjnoji a filin tashi da saukar jirage na Afrika ta Kudu
Fasinjnoji a filin tashi da saukar jirage na Afrika ta KuduHoto: Siphiwe Sibeko/REUTERS

Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya ta ce jirgin da ya sauka a birnin Lagos ya dauko fasinjoji 262 tare da jami'ai uku.

Tun daga watan Afrilu, an shafe makonni ana gudanar da zanga-zangar kin jinin bakin haure a sassan Afirka ta Kudu, lamarin da ya kara haifar da takaddama tsakanin 'yan kasar da ma'aikata 'yan kasashen waje.

Wasu 'yan kasar ta Afirka ta Kudu na zargin bakin haure da kwace musu guraben aiki, yayin da hukumomin kasar suka yi Allah wadai da zanga-zangar, suna mai bayyana ta a matsayin nuna kyamar baki.

Ministar harkokin wajen Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, ta ce shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar da umarnin kwaso 'yan Najeriya da ke ganin rayuwarsu na cikin hadari sakamakon ci-gaba da zama a Afirka ta Kudu.