1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
WasanniAfirka

Senegal da Mali sun kai wasan dab da na kusa da na karshe

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
January 4, 2026

Gasar cin kofin nahiyar Afirka AFCON: A ranar Litinin Najeriya za ta yi wasanta da Mozambique, da karfe 8 na dare.

https://p.dw.com/p/56ILb
Tawagar 'yan kasan kasar Mali, gabanin fafatawarsu da Tunisia
Tawagar 'yan kasan kasar Mali, gabanin fafatawarsu da TunisiaHoto: Ulrik Pedersen/NurPhoto/picture alliance

A gasar cin kofin nahiyar Afirka da ke wakana yanzu haka a kasar Morocco, Senegal ta samu damar shiga zagayen dab da na kusa da na karshe, bayan casa Sudan 3-1 da yammcin Asabar.

Haka zalika Mali ta samu zuwa wannan mataki, bayan doke Tunisia 3-2 a bugun daga kai sai mai tsaron raga, biyo bayan tashi 1-1 a mintuna 120.

A wannan Lahadi mai masaukin baki Morocco za ta fafata da Tanzania, da karfe 5 na yamma agogon Najeriya da Nijar.

Sai karawa tsakanin Afirka ta Kudu da Kamaru, da karfe 8 na dare.

A ranar Litinin Najeriya za ta yi wasanta da Mozambique, da karfe 8 na dare.