1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Senegal ta fara tsuke bakin aljihu saboda yakin Iran

April 4, 2026

Gwamnatin Senegal ta dakatar da yawan tafiye-tafiye ga jami'an gwamnati sakamakon tsadar makamashi da yakin Iran ya haifar.

https://p.dw.com/p/5BfFZ
Firanminstan kasar Ousmane Sonko
Firanminstan kasar Ousmane SonkoHoto: Abdel Majid Bziouat/AFP/Getty Images

Senegal kamar wasu kasashen Afirka da dama, na shigar da man fetur din da suke amfani da shi ne daga ketare, inda a yanzu rufe mashigin Hormuz ke tasiri sosai, wanda ke haifar da tsadar kaya a kasuwanni.

Karin bayani: Tsadar rayuwa a Senegal shekara guda cikin mulkin Faye

Firanminstan kasar Ousmane Sonko ya ce, gwamnatinsa a yanzu na daukar matakan rage kashe kudi, yana mai nuni da cewa kwarya-kwaryar kasafin kudin kasar na farko ya dogara ne kan farashin mai na dalar 62 kan kowacce ganga, wanda a yanzu ya ninka sau biyu sakamakon yakin Iran.

Ya kara da cewa ya soke tafiye-tafiye da dama da ya shirya yi, ciki har na ziyarar ayyuka da zai kai kasashen Nijar da Spain da kuma Faransa. A cewarsa, babu wani minista da zai yi tafiya zuwa ketare ba tare da wani babban dalili ba.