Sojojin Najeriya sun halaka Boko Haram 60
March 18, 2026
Duk da zuwan sojojin Amurka Najeriya don murkushe 'yan ta'adda, kungiyar ISWAP mai alaka da IS a yammacin Afirka, ta zafafa hare-hare kan sojoji da fararen hula a baya-bayan nan. Shugaban hafsoshin tsaron kasar Janar Olufemi Oluyede ya ziyarci birnin maiduguri bayan faruwar lamarin, inda ya zargi al'umma da rashin ba da hadin kai na kawo karshen matsalar. "Yawancin wadanda su ke kai wadannan hare-hare, 'yan wadannan jihohi ne."
Harin na zuwa ne bayan wasu hare-haren kunar bakin wake guda uku da ake kyautata zaton mayakan sun kai a ranar Litinin, inda suka kashe akalla mutane 23 tare da raunata wasu 108 a Maiduguri babban birnin Borno. Babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai hare-haren.
Tun a shekara ta 2009 kungiyar Boko Haram ta fara kaddamar da hare-hare a yankin arewa maso gabashin Najeriya domin tilasta musu tafsirin Shari'a, ko kuma shari'ar Musulunci. Tun daga lokacin ne kungiyar ta kara karfi, inda ta samu dubban mayaka daga bangarori daban-daban, ciki har da kungiyar ISWAP da ke yammacin Afirka, wacce ke samun goyon bayan kungiyar IS.
Rikicin dai ya fi karfin sojojin Najeriya, wadanda kuma ke fafatawa da sauran tashe-tashen hankula a arewacin kasar da ke fama da rikici. Sama da mutane 40,000ne aka kashe a Najeriya tun bayan barkewar rikicin Boko Haram a cewar bayanai daga Majalisar Dinkin Duniya.