1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan: An kashe gomman mutane a asibiti

March 22, 2026

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce ce a kalla mutane 64 ne suka mutu a harin da aka kai kan wani asibiti a gabashin birnin Darfur na Sudan.

https://p.dw.com/p/5ArqI
Rikicin Sudan na ci gaba da raba mutane da matsugunnansu
Rikicin Sudan na ci gaba da raba mutane da matsugunnansuHoto: AFP

Babban daractan Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, Tedros ​Adhanom Ghebreyesus ya ce harin ya rutsa da yara 13 da ma'aikatan jinya da kuma marasa lafiya da dama. A sakon da ya wallafa a sahfinsa na X, Tedros ya ce harin na asibitin koyarwa na Al Deain ya haifar da daina aiki a asibitin.

Karin bayani: Shin ana iya kawo karshen rikicin Sudan?

Ya kuma ce wasu mutum 89 sun jikkata a harin da ake zargin rundunar sojin kasar ce ta kai da jirgi mara matuki. Alkalumman WHO sun yi nuni da cewa, fiye da mutane 2,000 ne aka kashe a hare-hare fiye da 200 kan asibitoci tun bayan fara yakin basasa a Sudan a shekarar 2023.