Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sayi fom na neman takara a zaben 2027, lamarin da ya tayar da zazzafar muhawara. Shin zai ci gaba da mulki ne ko kuwa 'yan Najeriya za su kayar da shi a wanann zabe? Bashir Ahmad na APC da Zainab Buba Galadima ta ADC sune bakin da suka fafata shirinmu na Gaskiyar Magana na wannan makon wanda Zaharaddeen Umar Dutsen Kura ya jagoranta.