1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan gudun hijira na fama da matsalolin sauyin yanayi

Binta Aliyu Zurmi
November 10, 2025

Hukumar 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya UNCHR ta ce miliyoyin 'yan gudun hijira sun makale a cikin wani mummunan yanayi na rikici da bala'o'in muhalli.

https://p.dw.com/p/53MAv
Brasilien Belém 2025 | Luiz Inácio Lula da Silva beim Familienfoto des COP30-Gipfels
Hoto: Mauro Pimentel/AFP

Yayin da wasu mahalarta 50,000 daga kasashen duniya sama da 190 suka fara taron sauyin yanayi na COP30 a birnin Belem na kasar Brazil.

Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira ga taron da ya samar da kudade ga kasashe matalauta. Hukumar ta UNHCR, ta ce nan da shekaru 15 masu zuwa, yankunan da ke karbar kusan rabin ‘yan gudun hijira na duniya za su fuskanci mummunan tasirin sauyin yanayi. 

Rahoton hukumar ya ce kalubalen da sauyin yanayi ke haifarwa na kara yawan bukatun jin kai da kuma hadarin da mutane ke fuskanta na zama ‘yan gudun hijira. 

Kazalika rahoton ya ce zuwa tsakiyar wannan shekarar mutane miliyan 117 ne suka rasa matsugunansu sakamakon yaki da tashe-tashen hankula da kuma kauracewa gidajensu, inda uku daga cikin hudun su ke zaune a kasashen da ke fuskantar manyan bala'o'in muhalli.

 

Karin Bayani : Yawaitar 'yan gudun hijira daga Afirka inji UNCHR