Wani iftila'i ya kashe rayukan jama'a a kasar Kenya
November 1, 2025
Talla
'Yan sanda a yammacin kasar Kenya sun tabbatar da mutuwar akalla mutane 13 sakamakon zaftarewar kasa sanadiyyar ruwan sama mai yawa.
Lamarin ya faru ne a gundumar Elgeyo Marakwet, a yankin Rift Valley.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa 'yan sanda sun ce mutane 19 aka ceto su, yayin da har yanzu wasu ba a san inda suke ba.
Ma'aikatar kula da al'amuran cikin gida a Kenya, ta ce an aika jiragen sama na sojoji da 'yan sanda domin taimaka wa aikin ceto.
A ‘yan shekarun nan, irin wannan bala'in na sanadin daruruwan mutane a sassan Kenya daban-daban.
A makon nan ma, girgizar kasa a gabashin Yuganda makwabciyar Kenya ta hallaka akalla mutane 13, a cewar kungiyar agaji ta Red Cross.