SiyasaAfirka
Ana zaman zullumin siyasa a Tanzaniya
December 9, 2025
Talla
A birnin Dar es Salaam cibiyar kasuwancin kasar Tanzaniya ya kasance fayau ba kowa, bayan jami'an tsaro sun mamaye birnin bayan shirya zanga-zanga nuna adawa da gwamnati, biyo bayan tashe-tahsen hankula lokacin zaben kasar.
Yanayin da ake ciki
Tun farko Firaminista Mwigulu Nchemba ya bukaci mutane su zauna a gida domin guje wa rikicin da zai iya tashi sakamakon zanga-zangar da aka shirya.
A makon jiya 'yan sanda suka suka haramta duk wata zanga-zanga biyo bayan tashe-tahsen hankula na zabukan watan Oktoba da ya gabata, inda Shugaba Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben da kaso 98 cikin 100 na kuri'un da aka kada.
'Yan adawa sun ce fiye da mutane 1,000 suka halaka sakamakon rikicin zaben kasar ta Tanzaniya.