SiyasaAfirka
Bauna ta halaka mutane hudu masu kafin kifi a Kenya
January 4, 2026
Talla
Hukumomi a kasar Kenya sun tabbatar da mutuwar mutane hudu, sanadiyyar arangama da bauna a gabar kogin Naivasha, mai nisan kilomita 80 da Nairobi babban birnin kasar.
Sanarwar hukumomin ta ce mutane 14 ne suka je kamun kifi a kogin, cikin daren Juma'a, wanda ke hade da sanannen kogin nan mafi tsayi a duniya Rift Valley, daga nan ne baunar ta far musu.
Mahukuntan Kenya sun jima da haramta kamun kifi a kogin, tare da gargadin masu yawon bude ido su kauce wa shiga yankin cikin dare, musamman bakin kogin da kuma inda namun daji ke kiwo.