1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Bauna ta halaka mutane hudu masu kafin kifi a Kenya

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
January 4, 2026

Mutanen sun je kamun kifi a kogin Naivasha a daren Juma'a, wanda ke hade da kogin nan mafi tsayi a duniya Rift Valley.

https://p.dw.com/p/56J3p
Jami'an tsaron gandun dajin Kenya cikin kwale-kwale dauke da rakumin daji
Jami'an tsaron gandun dajin Kenya cikin kwale-kwale dauke da rakumin dajiHoto: Northern Rangelands Trust/AP Photo/picture alliance

Hukumomi a kasar Kenya sun tabbatar da mutuwar mutane hudu, sanadiyyar arangama da bauna a gabar kogin Naivasha, mai nisan kilomita 80 da Nairobi babban birnin kasar.

Sanarwar hukumomin ta ce mutane 14 ne suka je kamun kifi a kogin, cikin daren Juma'a, wanda ke hade da sanannen kogin nan mafi tsayi a duniya Rift Valley, daga nan ne baunar ta far musu.

Mahukuntan Kenya sun jima da haramta kamun kifi a kogin, tare da gargadin masu yawon bude ido su kauce wa shiga yankin cikin dare, musamman bakin kogin da kuma inda namun daji ke kiwo.