1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

CAF ta dakatar da kocin Senegal shiga gasar wasanni

January 29, 2026

CAF ta dakatar mai horas da kungiya da 'yan wasa tare kuma da cin tarar kasashen Senegal da Moroko, kan rashin da'a a AFCON.

https://p.dw.com/p/57ewq
Tawagar Senegal bayan lallasa Moroko da ci 1-0
Tawagar Senegal bayan lallasa Moroko da ci 1-0Hoto: Amr Abdallah Dalsh/REUTERS

A wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta bayyana cewa ta samu Pape Thiaw da laifin rashin dattako, a yayin wasan karshe da Senegal ta lallasa Maroko da ci 1-0, a ranar 18 ga watan Janairu. An kuma dakatar da shi shiga gasar wasanni biyar. CAF ta kuma haramta wa 'yan wasan Senegal da ke taka leda a Firimiyar Ingila, Iliman Ndiaye da Ismaila Sarr, shiga gasar wasanni biyu. An kuma ci tarar Hukumar Kwallon Kafa ta Senegal Dala $615,000.

Karin bayani:Senegal: Lashe gasar AFCON cikin Labarin Wasanni 

Daga bangaren Moroko kuwa, CAF ta dakatar da 'dan wasan gaba na kasar, Ismael Saibari, shiga wasanni uku da kuma tarar Dala $100,000, haka kuma an dakatar da kyaftin din Moroko Achraf Hakimi shiga wasanni biyu.
 

Tsallake zuwa bangare na gaba Rahotanni da Sharhuna