1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Ba za mu bari a kafa kasar Falasdinu ba - Netanyahu

September 11, 2025

Furucin na Netanyahu na zuwa ne bayan sanar da wani gagarumin aiki na gina gidaje 3,400 a Gabar Yamma da Kogin Jordan da Isra'ila ta mamaye.

https://p.dw.com/p/50Mfz
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanjahu
Firaministan Isra'ila Benjamin NetanjahuHoto: Menahem Kahana/AFP

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya sanar da cewa batun kafa kasar Falasdinu mai cikakken 'yanci ba zai taba yiwu ba, a yayin wanin biki da ya jagoranta domin rattaba hannu kan shirin ci gaba da mamaye yankin Gabar Yamma da Kogin Jordan.

A lokacin da yake wannan furuci mista Netanyahu ya nanata cewa Isra'ila za ta cika alkawarin da ta dauka na hana kafa kasar Falasdinu, tare da bayyana yankin na Gabar Yamma da Kogin Jordan a matsayin mallakin kasarsa.

Karin bayani: Abdallah II ya yi tir da mamaye Gabar Yamma da Kogin Jordan

A watan da ya shige ne dai Isra'ila ta amince da gudanar da wani gagarumin aiki na gina gidaje 3,400 a Gabar Yamma da Kogin Jordan da ta mamaye, matakin da Majalisar Dinkin Duniya da wasu shugabannin kasashen duniya suka yi Allah wadai da shi.