Isra'ila ta yi luguden wuta a yankin Rafah na Gaza
October 19, 2025
Rundunar sojin Isra'ila ta tabbatar da cewa ta yi barin wuta a birnin Rafah da ke kudancin Gaza a ranar Lahadi, bayan dakarunta sun fuskanci harin ‘yan bindiga.
A wata sanarwa da rundunar sojojin kasar ta fitar ta ce "da safiyar yau, ‘yan ta'adda sun bude wuta kan dakarun IDF da ke gudanar da aikin lalata cibiyoyin ta'addanci a yankin Rafah bisa sharuddan yarjejeniyar tsagaita wuta.”
Isra'ila ta yi barazanar komawa filin daga
Sanarwar ta kara da cewa dakarun Isra'ilar sun mayar da martani da hare-haren jiragen yaki da kuma harbi da manyan bindigogi a yankin Rafah domin kawar da barazanar.
An lalata wasu ramukan karkashin kasa da gine-ginen soji da aka gano ana amfani da su wajen ayyukan ta'addanci a cewar sanarwar ta Isra'ilawa.
Shin za a iya raba Hamas da ikon Zirin Gaza?
Wannan harin ya zo ne ana tsaka da aiwatar da yarjejeniyar tsagaitra wuta a Gaza wacce shugaban Amurka Donald Trump ya mika.