1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar masu fafutuka sauyin yanayi a taron COP30

Binta Aliyu Zurmi
November 16, 2025

Dubban mutane ne suka yi tattaki a birnin Belem na kasar Brazil a ranar Asabar a daidai lokacin da babban taron Majalisar Dinkin Duniya na COP30 ya kai rabinsa.

https://p.dw.com/p/53hCb
Brasilien Belém 2025 | Umweltaktivisten protestieren beim Auftakt der 30. UN-Klimakonferenz COP30
Hoto: Igor Mota/ZUMA/picture alliance

Taron gangamin, wanda masu shirya shi suka yi wa lakabi da "Tattakin Al'umma", ya zo ne bayan zanga-zangar da 'yan asalin kasar Brazil suka gudanar a farkon makon bude taron.

A ranar Asabar, masu zanga-zangar sun yi tattaki mai nisan kilomita hudu da rabi sanye da bakaken kaya, don nuna damuwa a kan yadda hayaki dake gurbata muhalli. 

Masu zanga-zangar sun jera akwatunan da ake daukar gawa guda uku dauke da kalaman "kwal" da "man fetur " da "gas."

Taron na COP30 a Belem wanda za a kammala shi a karshen mako, masu fafutukar kare muhallin na fatan za a samu ci gaba kan matakan da ake dauka don magance matsalar sauyin yanayi da illolinsa.

 

Karin Bayani: COP30: Ko kasashen duniya za su hada kai?