1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaIsra'ila

JD Vance na yin ziyara a Isra'ila

Abdourahamane Hassane
October 21, 2025

Mataimakin shugaban kasar Amurka JD Vance ya ce yana da matukar kwarin gwiwa cewa tsagaita bude wuta a Gaza zai ci gaba da kasancewa wani abun zahiri.

https://p.dw.com/p/52NP9
JD Vance
JD VanceHoto: Ammar Awad/REUTERS

JD vance wanda ya kai ziyara a Israi'la da nunfin karfafa shirin  tsagaita wutar, ya ce ba za su giciya wa'adi ba na ganin Hamas ta kwance damara mayakanta amma dai ta gaggauta yin haka.

Amurka da Isra'ila sun zargi Hamas, da karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta a zirin  Gaza, inda aka yi mummunar tashe-tashen hankula a ranar Lahadin da ta gabata wadanda suka yi barzana ga shirin zaman lafiyar.

Wannan tsagaita wutar da ya fara aiki a ranar 10 ga watan Oktoba, shi ne, na uku bayan shafe shekaru biyu ana yaki a Gaza,

sakamakon harin da Hamas ta kai wa Isra'ila a ranar 7 ga Oktoba, na shekara ta 2023 wanda ba a taba ganin irinsa ba.