1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar na tunawa da mulki da akidun Tandja Mamadou

Salissou Boukari MAB
November 25, 2025

'Yan Nijar na muhawara kan kyawawan akidun tsohon shugaban kasa Tandja Mamadou, wanda ya rasu shekaru biyar da suka gabata. Burin shi ne tunatar da al’umma irin kishin kasa da Tandja ya nuna duk da kalubalen juyin mulki

https://p.dw.com/p/54D1m
Marigayi Tandja Mamadou ya amfanar da Nijar a zamanin mulkinsa
Marigayi Tandja Mamadou ya amfanar da Nijar a zamanin mulkinsaHoto: DW/M. Kanta

Tsohon shugaban kasar Nijar Tandja Mamadou da ya rasu a ranar 24 ga Nuwamban 2020 yana dan shekaru 82 da haihuwa, ya zama wani abin kwatance da bege ga kasarsa ciki har da wadanda suka yaki tsarinsa na tazarce.

Saboda haka ne tun bayan rasuwarsa, kungiyar MPCR ta dan gwagwarmaya Nouhou Mahamadou Arzika da ya kalubalanci tsohon shugaban yake shirya taron tunawa da kyawawan dabi'un Tandja Mamadou a fannin son kasa da kyawawan dabi'u a fannin tafiyar da mulki.

Karin bayani:Nijar na zaman makokin Tandja Mamadou

Kamar yadda gwamnatin mulkin soja ke yi a halin yanzu, shi ma a lokacin mulkinsa tsohon shugaban kasa marigayi Tandja Mamadou, ya ja hankalin 'yan kasa zuwa ga neman na kansu maimakon mika hannun ga kasashen waje.

Shugaba Tandja ya sa Faransa kara farashin Uranium da take saya a Nijar
Shugaba Tandja ya sa Faransa kara farashin Uranium da take saya a NijarHoto: AP

Sannan Tandja ya jajirce wajen ganin an fitar da arziki na karkashin kasa kamar man fetur, lamarin da ke cike da darasi ga matasan da ke son koyon akidunsa.

An samu tsaffin abokan tafiya na tsohon shugaban kasa marigayi Tandja Mamadou, irin su Farfesa Katambe, da Issoufou Tamboura, da Hama Mamadou, da Ada Chefou da suka tabbatar da kyawawan halaye na mutunci da marigayi Tandja Mamadou ke nunawa, musamman rashin sa kudi a gaba a cikin harkokin rayuwarsa ta mulki. Falmata Moktar da ta halarci taron ta ce ta karu da wannan fanni.

Karin bayani: Sakin Mamadou Tandja ya samu martani

A halin yanzu, babban abin da ake son koyarwa ga manyan gobe shi ne, yin aiki tukuru da neman ilimi da kuma kare mutuncin kasar Nijar, tare da nesantar da kai daga kwadayi da ke jefa duk wani ma'aikaci ko mai rike da madafun iko cikin mayuwacin hali.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani