1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Rasha ta alkawarin daina saka 'yan Kenya aikin soja

Suleiman Babayo AH
March 16, 2026

Ministan harkokin wajen kasar Kenya ya ce Rasha ta yi alkawarin daina saka 'yan Kenya cikin yakin da ke faruwa tsakanin kasashen na Rasha da Ukraine.

https://p.dw.com/p/5AUL2
Musalia Mudavadi ministan harkokin wajen Kenya da Sergei Lavrov ministan harkokin wajen Rasha
Musalia Mudavadi ministan harkokin wajen Kenya da Sergei Lavrov ministan harkokin wajen RashaHoto: Sergei Fadeichev/TASS/picture alliance

Ministan harkokin wajen kasar Kenya, Musalia Mudavadi ya bayyana cewa kasar Rasha ta yi alkawarin daina saka 'yan Kenya aikin soja domin karawa a yakin da ke faruwa tsakanin kasashen na Rasha da Ukraine.

Abin da aka tattauna

Musalia Mudavadi ministan harkokin wajen Kenya da Sergei Lavrov ministan harkokin wajen Rasha
Musalia Mudavadi ministan harkokin wajen Kenya da Sergei Lavrov ministan harkokin wajen RashaHoto: Tatyana Makeyeva/AFP/Getty Images

Mudavadi ya shaida haka lokacin taron manema labarai a birnin Moscow na Rasha, inda yake ziyara bayan ganawa da Sergei Lavrov ministan harkokin wajen kasar ta Rasha.

Hukumomin tsaron Kenya sun yi kiyasin cewa akwai fiye da 'yan kasar ta Kenya 1,000 suke fagen-daga a wannan yaki tsakanin Rasha da Ukraine. Sannan Kenya ta kulla yarjejeniyar ganin 'yan kasar sun kara samun damar aiki a kasar ta Rasha.