1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

EU: Karshen dangantaka da Amurka ya zo?

Lateefa Mustapha Ja'afar
January 20, 2026

Shugabar Hukumar Gudanarwa ta Kungiyar Tarayyar Turai EU Ursula von der Leyen ta sha alwashin cewa, Turai za ta mayar da zazzafan martani a kan barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ke ci gaba da yi.

https://p.dw.com/p/577pa
Tarayyar Turai | EU | Davos |  Ursula von der Leyen | Martani | Amurka | Greenland
Shugabar Hukumar Gudanarwar Kungiyar Tarayyar Turai EU, Ursula von der LeyenHoto: Fabrice Coffrini/AFP

Ursula von der Leyen ta ce barazanar da Shugaba Donald Trump ke kara yi, ba za ta haifar da komai ba sai dai bai wa makiya dama da kuma dakile kokarin da suke na yakar abubuwan da ke yin barazana ga zaman lafiya. A cewarta, za su mayar da martani ba tare da fargaba ba kuma cikin hadin kai. Shugabar Hukumar Gudanarwa ta Kungiyar Tarayyar Turan ta bayayana hakan ne a jawabin da ta gabatar yayin taron tattalin arziki da ke gudana a birnin Davos na kasar Switzerland, inda ta ce: "Abin da nake so na bayyana shi ne, idan wannan sauyin ya kasance na din-din-din, to tilas Turai ma ta sauya na din-din-din. Lokaci ne da za mu yi amfani da wannan dama, mu samar da sabuwar Turai mai 'yanci."