Taron sauyin yanayi na daukan hankali
November 11, 2025
Duk da gwamnatin Amurka karkashin Shugaba Donald Trump ba ta tura wakilai zauren taron Majalisar Dinkin Duniya kan kare muhalli ba, amma an samu gwamnonin jihohin California da New Mexico daga kasar ta Amurka wadanda suke cikin mahalarta taron, kuma suna cikin jihohin kasar ta Amurka masu karfin tattalin arziki. Akwai fata mahalarta taro su cimma manufofin da za su taimaka wajen magance matsalolin na sauyin yanayi a duniya.
Burin taron
Taron da ke gudana a birnin Belem na kasar Brazil na neman magance matsalolin sauyin yanayi bisa matakan hadin kai tsakanin kasashen domin dakile matsalolin gurbatar muhallin dan Adam.
Kana ana tantance yuwuwar bai wa kasar Habasha daga nahiyar Afirka damar daukan nauyin taron na shekara ta 2027, yayin da ake takaddama kan kasar da za ta dauki nauyin taron na shekara mai zuwa ta 2026 tsakanin kasashen Australiya da Turkiyya.