Amurka ta gargadi China kan yi wa Taiwan barazanar soji
January 2, 2026
Kakakin ma'aikatar harkakin wajen Amurka Tommy Pigott ya fitar da sanarwa a ranar Alhamis, wadda a cikinta Washington ta yi kiran Beijing da ta kai zuciya nesa tare da dakatar da barazanar soji da take yi wa Taiwan.
Sanarwar ta bayyana atisayen sojoji da China ta yi a baya-bayan nan a kusa da Taiwan a matsayin abin da ke kara rura tada jiyoyin wuya, sannan kuma ta shawarci Beijing ta hau tebirin tattaunawa da mahukutan Taiwan.
Har wa yau Washington ta ce tana goyon bayan zaman lafiya a mashigin tekun Taiwan, kana kuma tana adawa da duk wani yin gaban kai ta hanyar barazanar soji ko kuma matsin lamba.
China dai da ke ikirarin cewa tsibirin Taiwan wani yanki ne na kasarta, ta gudanar da gagarumin atisayen soji a farko da tsakiyar wannan mako, lamarin da shugaban Amurka Donald Trump ta bayyana a matsayin abin damuwa.