Shawarar Trump ce mafita ga Gaza?
September 24, 2025
Ganawar tasu na zuwa ne, a daidai lokacin da ake taron Majalisar Dinkin Duniya zagaye na 80 ake kuma samun karin kasashen duniya da suke amincewa da kafuwar kasar Falasdinu mai cikakken 'yanci.
Wacce rawa wadanna kasashe za su taka a Gaza?
Shugaban Amurka Donald Trump dai ya gana da manyan Kasashen Larabawa da na Musulmin duniya bakwai da suka hadar da Saudiyya da Masar da Katar da Jordan da Turkiyya da Pakistan da kuma Indonosiya.
Yayin ganawar tasu Trump ya ce: "Dole ne mu kawo karshen yaki a Gaza a kuma saki ilahirin wadanda ake tsare da su......."
Matsin lamba da ga Hamas da kwace iko daga hannunta
Daftarin kudirin ya nemi kasashen su matsawa Hamas lamba ta sako wadanda take tsare da su nan take, kana kasashen su kafa rundunar tsaro da za ta maye gurbin dakarun Isra'ila da za su fice daga ilahirin Zirin na Gaza.
Ya kuma dorawa Kasashen na Larabadawa da na Musulmi alhakin sake gina Gaza, kana su kafa gwamnatin Falalsdinawa da ba za ta kunshi kungiyar Hamas ba.